Zanga-zangar Ali Must Go ta shekarar 1978 ko Rikicin dalibai na shekarar 1978 dai zanga-zangar dalibai ne a Najeriya biyo bayan ƙarin kuɗaɗe-(na makaranta).[1] An bayyana zanga-zangar a matsayin ɗaya daga cikin tashin hankalin dalibai a Najeriya[2] kuma ya haifar da rikicin siyasa mafi girma na shekarar 1975-1979 a mulkin sojan Mohammed/Obasanjo.[3]